====== Fauziya D. Sulaiman ======
{{ cast_and_crew:writer_fauziya_d_sulaiman.png?228 }} \\ **Occupation** [[:cast_and_crew?dataflt=occupation%3DWriter|Writer]] \\ **Hometown** Fagge, Kano, Nigeria
Fauziyya D. Sulaiman wadda aka fi sani da Matar Bello Q far Q an haife ta a unguwar Fagge a Shekarar 1981 ta yi karatuna na Firamare a Makarantar Festival Primary School, daga nan wuce makarantar ‘yammata ta kwana Government Girls Secondary School ‘Yar gaya a shekara ta 1993, bayan ta kammala karatunta na Jiniya ta koma Makarantar Government Girls College Dala ta karasa karatunta daga 1995 zuwa 1998. Daga nan ta yi aure a shekara ta 1999. A shekara ta 2003 ta koma karatu a Makarantar College of Health Sciences, School of Hygiene in da ta yi Diploma a kan Assistant Nutritionist. Daga nan ta yi Certificate a Makarantar School of Management, akan Hotel and Catering Services.
\\
\\
\\
\\
A game da rubutu kuwa ta fara rubuta littafi a shekarar 2002, in da littafi na farko mai suna Me na yi mata?. Daga nan ta ci gaba da rubuta littafi da suka hada da:
- [[film/Kishin Banza]]
- [[film/Guduna Ake yi]]
- [[film/Rayuwar ‘Ya Mace]]
- [[film/Mece ce Rayuwa]]
- [[film/Burin Raina]]
- [[film/Karshen Wahala]]
- [[film/Labarin Zuciya]]
- [[film/Matsalar Mace]]
- [[film/Mijin Uwa]]
- [[film/Auren Kudi]]
- [[film/Duk Abinda Namiji Ya yi]]
Fauziyya mamba ce a Kungiyar Marubuta ta Najeriya reshen jihar Kano kuma tana rike da mukamin jami’a a majalisar gudanarwa ta Kungiyar tun watan Maris na 2009 har zuwa 2010. Daga nan aka sake zabenta a dai wannan mukami daga watan Maris na 2010 har zuwa watan Maris na 2012 insha Allahu.
Daga/by Professor Yusuf M. Adamu at Wednesday, March 31, 2010 http://marubutanhausa.blogspot.com/2010/03/fauziyya-d-sulaiman.html
===== Hira da AREWA24 =====
\\
Published by [[producer/arewa24]]'s [[film/kundin kannywood]] on Dec 5, 2014\\
===== Share this page =====