User Tools

Site Tools


writer:fauziya_d_sulaiman.

Fauziya D. Sulaiman


Occupation Writer
Hometown Fagge, Kano, Nigeria

Fauziyya D. Sulaiman wadda aka fi sani da Matar Bello Q far Q an haife ta a unguwar Fagge a Shekarar 1981 ta yi karatuna na Firamare a Makarantar Festival Primary School, daga nan wuce makarantar ‘yammata ta kwana Government Girls Secondary School ‘Yar gaya a shekara ta 1993, bayan ta kammala karatunta na Jiniya ta koma Makarantar Government Girls College Dala ta karasa karatunta daga 1995 zuwa 1998. Daga nan ta yi aure a shekara ta 1999. A shekara ta 2003 ta koma karatu a Makarantar College of Health Sciences, School of Hygiene in da ta yi Diploma a kan Assistant Nutritionist. Daga nan ta yi Certificate a Makarantar School of Management, akan Hotel and Catering Services.





A game da rubutu kuwa ta fara rubuta littafi a shekarar 2002, in da littafi na farko mai suna Me na yi mata?. Daga nan ta ci gaba da rubuta littafi da suka hada da:

Fauziyya mamba ce a Kungiyar Marubuta ta Najeriya reshen jihar Kano kuma tana rike da mukamin jami’a a majalisar gudanarwa ta Kungiyar tun watan Maris na 2009 har zuwa 2010. Daga nan aka sake zabenta a dai wannan mukami daga watan Maris na 2010 har zuwa watan Maris na 2012 insha Allahu.

Daga/by Professor Yusuf M. Adamu at Wednesday, March 31, 2010 http://marubutanhausa.blogspot.com/2010/03/fauziyya-d-sulaiman.html

Hira da AREWA24


Published by AREWA24's Kundin Kannywood on Dec 5, 2014

Share this page

writer/fauziya_d_sulaiman.txt · Last modified: 2016/05/29 22:53 by admin